Naja’atu Mohammed, ta bayyana shirin da ‘yan Arewa ke yi na maye gurbin dan takarar Shugaban kasa na Jam’iyyar APC, Bola Tinubu, da abokin takararsa, Kashim Shettima. Naja’atu ta yi ikirarin cewa wasu ’yan Arewa ne ke kira ga Tinubu ya ci gaba da cewa Shettima zai maye gurbinsa idan lafiyarsa ta tabarbare kuma ya gaza. Da take magana da jaridar ThisDay, Naja’atu ta ce: “Suna so ne kawai su tura shi ya zama shugaban kasa. Ko da bai dace da sha’awarsa ba.” “Wasu mutane daga Maiduguri sun kira ni yau suna tambayar, ‘Hajiya, me ya sa kika yi haka? Yanzu kina sukar kudirinmu. Danmu zai zama shugaban kasa, amma kina magana irin wannan? Bayan haka ma, yanzu dubi Tinubu; ba zai iya ba. Mu duka don Kashim muke yi. Ba ki kyautata mana ba.” Naja’atu ta kuma yi ikirarin cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari bai damu da tattalin arziki, tsaro, ko kuma wanda zai gaje shi a matsayin shugaban kasa ba. Ta bayyana cewa, duk da bayanan da aka samu daga dukkan hukumomin tsaro, shugaban bai damu da