Rahotonni na cewa 'yan bindigar sun kashe wasu manoma shida a yankin Riyom, yayin da waso 10 suka rasa rayukansu a yankin Mangu ranar Talata.
Maharan sun ƙaddamar da hari kan garuruwan biyu inda suka kashe mutane tare da cinna wuta kan gidaje masu yawa.
Mai magana da yawun gwamnan jihar Mista Gyan Bere ya shaida wa BBC cewa an shirya tawagar jami'an tsaro da ta ƙunshi sojoji da 'yan sanda domin kare garuruwan tare da farauto maharan.
Ya ƙara da cewa gwamnan jihar ya gaji irin waɗannna hare-hare ne daga tsohuwar gwamnatin jihar.
''Gwamna na ganawa da shugabannin tsaro da jagororin al'umma domin magance matsalar da ake ciki, da kuma maido da zaman lafiya a faɗin jihar'', in ji shi.
Mista Bere ya ce gwamnatin jihar ba ta kai ga gano waɗanda ke kai hare-haren ba.
Sai dai kafofin yaɗa labaran ƙasar na ruwaito cewa hare-haren ramuwar gayya tsakanin makiyaya da manoma ne ke yawan haddasa irin waɗannan kashe-kashe a jihar.
Rahotonni na cewa kusan mutum 200 ne suka mutu tun watan Mayu a rikice-rikice masu alaƙa da manoma da makiya.
Comments
Post a Comment
Rubuta Sharhinku