#Attribution1 {display; none;} Skip to main content

Juma'a 23, Yuni, 2023

Jami'an tsaro na farautar 'yan bindigar da suka kashe mutum 15 a Plateau

Hukumomin jihar Plateau da ke tsakiyar Najeriya sun ce jami'an tsaro na neman 'yan bindigar da suka kai hare-hare kan wasu garuruwa biyu, tare da kashe a ƙalla mutum 15 a jihar.

Rahotonni na cewa 'yan bindigar sun kashe wasu manoma shida a yankin Riyom, yayin da waso 10 suka rasa rayukansu a yankin Mangu ranar Talata.

Maharan sun ƙaddamar da hari kan garuruwan biyu inda suka kashe mutane tare da cinna wuta kan gidaje masu yawa.

Mai magana da yawun gwamnan jihar Mista Gyan Bere ya shaida wa BBC cewa an shirya tawagar jami'an tsaro da ta ƙunshi sojoji da 'yan sanda domin kare garuruwan tare da farauto maharan.

Ya ƙara da cewa gwamnan jihar ya gaji irin waɗannna hare-hare ne daga tsohuwar gwamnatin jihar.

''Gwamna na ganawa da shugabannin tsaro da jagororin al'umma domin magance matsalar da ake ciki, da kuma maido da zaman lafiya a faɗin jihar'', in ji shi.

Mista Bere ya ce gwamnatin jihar ba ta kai ga gano waɗanda ke kai hare-haren ba.

Sai dai kafofin yaɗa labaran ƙasar na ruwaito cewa hare-haren ramuwar gayya tsakanin makiyaya da manoma ne ke yawan haddasa irin waɗannan kashe-kashe a jihar.

Rahotonni na cewa kusan mutum 200 ne suka mutu tun watan Mayu a rikice-rikice masu alaƙa da manoma da makiya.

Comments

Popular posts from this blog

Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam

Wata kotu a Birtaniya ta samu ɗan majalisar dattijan Najeriya, Ike Ekweremadu da matarsa da laifin yunkurin safarar sassan ɗan adam. Shari'ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun. Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda. Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25. Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata. Matashin da aka so amfani da ƙodar tasa, wani mai ƙaramar sana’a ne a birnin Legas. An kai shi Birtaniya ne a bara domin gudanar da aiki a asibitin Royal Free Hospital da ke biornin London. Ya ce an yi alƙawarin samar masa aiki a Birtaniya saboda taimakon da zai yi, sai dai ya ce ya gane cewa ana masa shigo-shigo ba zurfi ne bayan tattaunawa da likitoci a ƙasar ta Birtaniya. Duk da cewa ba laifi ba ne bayar da g

DEEJARH BERVER ENTERPRISES

DAMA GARE KU MATA!!! DAMA GARE KU MATA MASU BUKATAR KOYON GIRKE-GIRKEN KWALAM DA MAKULASHE, KUNA ZAUNE TSAF DAGA CIKIN GIDAJENKU. DEEJARH BERVER TA SHIRYA TSAF DOMIN KOYO MUKU HADADDUN GIRKE-GIRKE, YADDA ZAKI SARRAFA ABINCI DA LEMOKA DA HADIN SALAD DA SNACKS HAR GUDA 40, TAMKAR KUNA GABANTA. ZA A GABATAR DA KOYARWAR TA CIKIN WAYOYIN HANNUNKU WATO TSARIN ONLINE LECTURE MAI DAUKE DA HOTON VIDEO DA RUBUTU DALLA-DALLA AKAN TA CIKIN MANHAJAR WHATSAPP DA TELEGRAM. KOWA NA DA DAMAR YIN TAMBAYA KO TATTAUNAWA DA MALAMA A SIRRANCE. KU DAI KU YI RIJISTA A YAU AKAN KUDI NAIRA 2,500 KACAL. ZA MU FARA KOYARWA RANAR 18 March, 202. DOMIN KARIN BAYANI KIRA WANNAN LAMBAR 09079274454

Jadawalin Lokutan Sahur Da Buda Baki A Birnin Kano