Shari'ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun.
Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda.
Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25.
Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata.
Matashin da aka so amfani da ƙodar tasa, wani mai ƙaramar sana’a ne a birnin Legas.
An kai shi Birtaniya ne a bara domin gudanar da aiki a asibitin Royal Free Hospital da ke biornin London.
Ya ce an yi alƙawarin samar masa aiki a Birtaniya saboda taimakon da zai yi, sai dai ya ce ya gane cewa ana masa shigo-shigo ba zurfi ne bayan tattaunawa da likitoci a ƙasar ta Birtaniya.
Duk da cewa ba laifi ba ne bayar da gudumawar ƙoda, to amma hakan kan zama laifi idan har za a biya wanda zai bayar da ƙodar.
A lokacin da aka gane cewar ba za a iya amfani da ƙodar mutumin ba, kotun ta gano cewa iyalan na Ekweremadu sun mayar da hakalinsu wurin samun wani mutumin na daban a ƙasar Turkiyya.
Sai iyalan na Ekweramadu waɗanda ke da gida a birnin London sun musanta tuhumar da aka yi masu.
Comments
Post a Comment
Rubuta Sharhinku