An bayyana cewa, dage zaben ya biyo bayan gazawar hukumar ta sake fasalin na’urorin tantance masu kada kuri’a (BVAS) da aka yi amfani da su a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu, domin samun damar yin amfani da su a zaben jihar.
Majiya mai tushe ta shaida wa Taskar Lafazi cewa hukumar gudanarwar hukumar na gudanar da wani taro a halin yanzu, inda ta ke nazarin ko dai ranar 18 ga watan Maris ko 25 ga watan Maris domin gudanar da zaben.
Wata kotu a Birtaniya ta samu ɗan majalisar dattijan Najeriya, Ike Ekweremadu da matarsa da laifin yunkurin safarar sassan ɗan adam. Shari'ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun. Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda. Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25. Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata. Matashin da aka so amfani da ƙodar tasa, wani mai ƙaramar sana’a ne a birnin Legas. An kai shi Birtaniya ne a bara domin gudanar da aiki a asibitin Royal Free Hospital da ke biornin London. Ya ce an yi alƙawarin samar masa aiki a Birtaniya saboda taimakon da zai yi, sai dai ya ce ya gane cewa ana masa shigo-shigo ba zurfi ne bayan tattaunawa da likitoci a ƙasar ta Birtaniya. Duk da cewa ba laifi ba ne bayar da g
Comments
Post a Comment
Rubuta Sharhinku