#Attribution1 {display; none;} Skip to main content

Juma'a 23, Yuni, 2023

Amurka ta ƙwace $53m daga hannun Diezani bayan kama ta da laifi

Ma'aikatar shari'a ta Amurka ta cimma matsaya kan wasu shari'u biyu da suka buƙaci ƙwace wasu manyan kadarori na alfarma da aka samar da su a ƙasar ta hanyar laifukan almundahanar kuɗaɗe.

Wasu takardu daga ma'aikatar shari'ar ƙasar sun nuna cewa batun ya shafi tsohuwar ministar albarkatun man fetur ta Najeriya Diezani Alison-Madueke da wasu abokan kasuwancinta biyu Kolawole Akanni Aluko da Olajide Omokore.

Da wannan mataki a yanzu ma'aikatar shari'ar ƙasar ta ce ta ƙwace kuɗin da ya kai dala miliyan 53.1, ƙimar kuɗin kadarorin idan aka sayar da su.

Takardun kotun sun nuna cewa daga shekarar 2011 zuwa 2015 Diezani wadda a lokacin take ministar man fetur a Najeriya ta karɓi cin hanci daga abokan kasuwancinta.

Wadda ita kuma Diezani ta riƙa bai wa kamfanoninsu manyan kwangilolin man fetur.

Ma'aikatar shari'ar Amurkan ta ce an yi amfani da kuɗaden da aka biya a matsayin cin hancin da yawansu ya kai sama da dala miliyan 100, wajen sayan manyan kadarori a Amurka, ciki har da rukunin gidaje a California da New York da kuma Galactica Star.

Comments

Popular posts from this blog

Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam

Wata kotu a Birtaniya ta samu ɗan majalisar dattijan Najeriya, Ike Ekweremadu da matarsa da laifin yunkurin safarar sassan ɗan adam. Shari'ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun. Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda. Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25. Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata. Matashin da aka so amfani da ƙodar tasa, wani mai ƙaramar sana’a ne a birnin Legas. An kai shi Birtaniya ne a bara domin gudanar da aiki a asibitin Royal Free Hospital da ke biornin London. Ya ce an yi alƙawarin samar masa aiki a Birtaniya saboda taimakon da zai yi, sai dai ya ce ya gane cewa ana masa shigo-shigo ba zurfi ne bayan tattaunawa da likitoci a ƙasar ta Birtaniya. Duk da cewa ba laifi ba ne bayar da g

DEEJARH BERVER ENTERPRISES

DAMA GARE KU MATA!!! DAMA GARE KU MATA MASU BUKATAR KOYON GIRKE-GIRKEN KWALAM DA MAKULASHE, KUNA ZAUNE TSAF DAGA CIKIN GIDAJENKU. DEEJARH BERVER TA SHIRYA TSAF DOMIN KOYO MUKU HADADDUN GIRKE-GIRKE, YADDA ZAKI SARRAFA ABINCI DA LEMOKA DA HADIN SALAD DA SNACKS HAR GUDA 40, TAMKAR KUNA GABANTA. ZA A GABATAR DA KOYARWAR TA CIKIN WAYOYIN HANNUNKU WATO TSARIN ONLINE LECTURE MAI DAUKE DA HOTON VIDEO DA RUBUTU DALLA-DALLA AKAN TA CIKIN MANHAJAR WHATSAPP DA TELEGRAM. KOWA NA DA DAMAR YIN TAMBAYA KO TATTAUNAWA DA MALAMA A SIRRANCE. KU DAI KU YI RIJISTA A YAU AKAN KUDI NAIRA 2,500 KACAL. ZA MU FARA KOYARWA RANAR 18 March, 202. DOMIN KARIN BAYANI KIRA WANNAN LAMBAR 09079274454

Jadawalin Lokutan Sahur Da Buda Baki A Birnin Kano