#Attribution1 {display; none;} Skip to main content

Juma'a 23, Yuni, 2023

PDP ta maye gurbin Iyioricha Ayu bayan dakatar da shi

Iyioricha Ayu lokacin da ya lashe zaben shugabancin jam'iyyar ta PDP. Iyioricha Ayu lokacin da ya lashe zaben shugabancin jam'iyyar ta PDP.

Kwamitin ayyuka nababbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya, ya maye gurbin shugaban jam’iyyar Sanata Iyioricha Ayu.

A wani taron gaggawa da jam’iyyar ta yi a ranar Talata, kwamitin ya amince da umarnin babbar kotun jihar Benue, wadda ta haramta wa Ayu bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar.

Da yake jawabi ga manema labarai a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya ce bayan yin nazari da kyau da umarnin kotu da kuma bin sashe na 45 (2) na kundin tsarin mulkin PDP da aka yi wa gyara a 2017, kwamitin ya yanke shawarar cewa Mataimakin Shugaban shiyyar Arewa, Ambasada Umar Ilyya Damagum shine zai rike shugabancin jam’iyyar.

Rikicin jam’iyyar bayan zaben kasar, ya dauki wani sabon salo a ranar Lahadin da ta gabata lokacin da masu ruwa da tsaki na gundumar Igyorov a karamar hukumar Gboko ta jihar Binuwai suka dakatar da Ayu bisa zargin yiwa jam’iyyar zagon kasa.

An dauki matakin ne kwanaki kadan bayan kwamitin jam'iyyar ya kai gwamnan jihar Benuwe Samuel Ortom gaban kwamitin ladabtarwa tare da dakatar da wani tsohon gwamnan jihar Ekiti Ayodele Fayose da tsohon shugaban majalisar dattawa Anyim Pius Anyim da dai sauransu.

Dakatar da Ayu ya biyo bayan kuri'ar rashin amincewa da shi da shugabannin gundumar suka yi masa a karshen taron nasu.

Sakatariyar gundumar, Vangeryina Dooyum, a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun 12 daga cikin mambobi 17 na gundumar, ta ce an cimma matsayar dakatar da shugaban na kasa ne bayan da shugabannin suka yi nazari a kan rawar da ya taka a karshen babban zaben 2023.

Ayu ya bayyana matakin a matsayin zancen wofi, inda ya ce duk wani tsagi na jam’iyya ko kwamitin zartarwa na jam’iyyar a matakin gunduma ko Jiha ba za ta iya daukar wani mataki na ladabtarwa ga duk wani dan kwamitin zartarwa na jam’iyyar na kasa ba.

Amma daga baya wata babbar kotun jihar Benue ta hana shi bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar PDPn na kasa.

Comments

Popular posts from this blog

Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam

Wata kotu a Birtaniya ta samu ɗan majalisar dattijan Najeriya, Ike Ekweremadu da matarsa da laifin yunkurin safarar sassan ɗan adam. Shari'ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun. Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda. Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25. Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata. Matashin da aka so amfani da ƙodar tasa, wani mai ƙaramar sana’a ne a birnin Legas. An kai shi Birtaniya ne a bara domin gudanar da aiki a asibitin Royal Free Hospital da ke biornin London. Ya ce an yi alƙawarin samar masa aiki a Birtaniya saboda taimakon da zai yi, sai dai ya ce ya gane cewa ana masa shigo-shigo ba zurfi ne bayan tattaunawa da likitoci a ƙasar ta Birtaniya. Duk da cewa ba laifi ba ne bayar da g

DEEJARH BERVER ENTERPRISES

DAMA GARE KU MATA!!! DAMA GARE KU MATA MASU BUKATAR KOYON GIRKE-GIRKEN KWALAM DA MAKULASHE, KUNA ZAUNE TSAF DAGA CIKIN GIDAJENKU. DEEJARH BERVER TA SHIRYA TSAF DOMIN KOYO MUKU HADADDUN GIRKE-GIRKE, YADDA ZAKI SARRAFA ABINCI DA LEMOKA DA HADIN SALAD DA SNACKS HAR GUDA 40, TAMKAR KUNA GABANTA. ZA A GABATAR DA KOYARWAR TA CIKIN WAYOYIN HANNUNKU WATO TSARIN ONLINE LECTURE MAI DAUKE DA HOTON VIDEO DA RUBUTU DALLA-DALLA AKAN TA CIKIN MANHAJAR WHATSAPP DA TELEGRAM. KOWA NA DA DAMAR YIN TAMBAYA KO TATTAUNAWA DA MALAMA A SIRRANCE. KU DAI KU YI RIJISTA A YAU AKAN KUDI NAIRA 2,500 KACAL. ZA MU FARA KOYARWA RANAR 18 March, 202. DOMIN KARIN BAYANI KIRA WANNAN LAMBAR 09079274454

Jadawalin Lokutan Sahur Da Buda Baki A Birnin Kano