#Attribution1 {display; none;} Skip to main content

Juma'a 23, Yuni, 2023

Martanin jam'iyyu kan kammala zabuka

A Najeriya, tuni wasu `yan takara da ke dakon a kammala zabensu suka yi maraba da sanarwar Hukumar Zabe mai Zaman Kanta ta kasar INEC, wadda ta sanya ranar 15 ga watan Afrilu mai zuwa don kammala zaben gwamnoni da na`yan majalisun dokoki a wasu sassan kasar.

Sanarwa INEC din ta kawo karshen dogon zaman jiran da al`umomin yankunan da zaben ya shafa da kuma `yan takara ke yi.

Jihar Adamawa da Kebbi su ne jihohi biyu rak da ba a kammala zaben gwamna ba a Najeriyar.

Tsohon ministan lafiya da harkokin wajen Najeriya kuma jigo a kwamitin yakin neman zaben gwamna Fintiri na jam’iyyar PDP a Adamawa, Dr Idi Hong, ya shaida wa BBC cewa, tsayar da ranar sake zaben za ta ba su damar sake shiri har su sake zuwa wuraren da aka soke zabensu don sake yada manufofinsu.

Ya ce, “ Dama mu jam’iyyar PDP masu bin doka ne don haka za mu jira ranar da aka tsayar don sake zaben nan, idan aka yi zaben nan za a gane bambanci.”

A jihar Kebbi ma zaben gwamnan da aka yi a zagayen farko, kamar yadda hukumar zabe ta ce bai kammala ba, saboda ratar kuri`a 45,000 da doriya da dan takarar gwamna na jam`iyyar APC ya bai wa takwaransa na PDP ba ta zarta yawan masu katin zabe 91, 000 da doriya da ke yankunan da aka soke zabe ba.

Kakakin kwamitin yakin neman zaben dan takarar gwamna na jam`iyyar APC, Alhaji Kabiru Sani Jahin, ya shaida wa BBC cewa suna maraba da ranar kammala zaben.

Ya ce, “ Ya mana dadi kwarai da gaske saboda mu ‘yan jam’iyyar APC mu ke kan gaba a zaben da aka yi, don haka mun fi kowa farin cikin a sake wannan zaben.”

Bayan zaben gwamnan da za a kammala a jihohi biyun, za kuma a karasa na`yan majalisar dattawa a gundumar sanata biyar a wasu sassan Najeriyar.

Sannan akwai kujerar majalisar wakilai 31 da su ma za a kammala zaben nasu.

Sai kuma kujerar majalisar dokoki ta jiha guda 58 da su ma suke dakon a karasa zaben nasu.

Comments

Popular posts from this blog

Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam

Wata kotu a Birtaniya ta samu ɗan majalisar dattijan Najeriya, Ike Ekweremadu da matarsa da laifin yunkurin safarar sassan ɗan adam. Shari'ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun. Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda. Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25. Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata. Matashin da aka so amfani da ƙodar tasa, wani mai ƙaramar sana’a ne a birnin Legas. An kai shi Birtaniya ne a bara domin gudanar da aiki a asibitin Royal Free Hospital da ke biornin London. Ya ce an yi alƙawarin samar masa aiki a Birtaniya saboda taimakon da zai yi, sai dai ya ce ya gane cewa ana masa shigo-shigo ba zurfi ne bayan tattaunawa da likitoci a ƙasar ta Birtaniya. Duk da cewa ba laifi ba ne bayar da g

DEEJARH BERVER ENTERPRISES

DAMA GARE KU MATA!!! DAMA GARE KU MATA MASU BUKATAR KOYON GIRKE-GIRKEN KWALAM DA MAKULASHE, KUNA ZAUNE TSAF DAGA CIKIN GIDAJENKU. DEEJARH BERVER TA SHIRYA TSAF DOMIN KOYO MUKU HADADDUN GIRKE-GIRKE, YADDA ZAKI SARRAFA ABINCI DA LEMOKA DA HADIN SALAD DA SNACKS HAR GUDA 40, TAMKAR KUNA GABANTA. ZA A GABATAR DA KOYARWAR TA CIKIN WAYOYIN HANNUNKU WATO TSARIN ONLINE LECTURE MAI DAUKE DA HOTON VIDEO DA RUBUTU DALLA-DALLA AKAN TA CIKIN MANHAJAR WHATSAPP DA TELEGRAM. KOWA NA DA DAMAR YIN TAMBAYA KO TATTAUNAWA DA MALAMA A SIRRANCE. KU DAI KU YI RIJISTA A YAU AKAN KUDI NAIRA 2,500 KACAL. ZA MU FARA KOYARWA RANAR 18 March, 202. DOMIN KARIN BAYANI KIRA WANNAN LAMBAR 09079274454

Jadawalin Lokutan Sahur Da Buda Baki A Birnin Kano