Rundunar ƴan sandan jihar Gombe ta ce ta kama wani matashi mai shekara 38 malamin Islamiyya bisa zargin lalata da wasu yara mata guda huɗu duka ƴaƴan mutum ɗaya.
Rundunar ta tabbatar da kama malamin kamar yadda mai magana da yawunta, DSP Mahid Mu’azu Abubakar ya yi wa BBC ƙarin bayani.
A cewarsa yaran da abin ya rutsa da su ƴan shekara 12 ne da tara da kuma takwas.
"Ba asalin malaminsu ba ne, yana zaune ne a makarantar Islamiyya ɗin, idan suka zo biya karatu, babban malami zai ce su je wajen wanda ake tuhuma da laifin domin su biya masa, sai yake amfani da wannan dama wajen yin lalata da yaran." in ji kakakin rundunar.
Ya ce an ɗauki lokaci matashin yana cin zarafin ɗaliban kasancewar yaran ƙanana ne da ba sa iya yi wa iyayensu bayanin abin da ke faruwa da su a makaranta.
Comments
Post a Comment
Rubuta Sharhinku