Jami’an ‘yan sanda a jihar Imo sun ceto ma’aikatan wucin-gadi na hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) guda goma sha bakwai a jihar Imo.
Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba suka yi garkuwa da jami’an hukumar ta INEC da aka tura zuwa mazabu goma 19 a karamar hukumar Ideato ta Kudu, a kan hanyarsu ta zuwa wajen da za su yi aiki daban-daban.
Sai dai an rawaito cewa ‘yan sandan sun yi gaggawar ceto su daga baya.
Da yake magana da manema labarai a ranar Asabar, mai magana da yawun hukumar ta INEC na jihar, Dr. Chineye Chijioke-Osuji, ya tabbatar da ceto jami’an.
Chijioke-Osuji, ya ce an ceto jami’an zaben ne ba tare da kayayyakin zabe ba da kuma na'urar (BVAS).