Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da mutum 17 daga cikin sunaye 19 da gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf ya aike mata domin amincewa da naɗinsu a matsayin kwamishinoni a jihar.
Majalisar ta amince da sunayen ne a zamanta na ranar Alhamis, ƙarƙashin jagorancin kakakin majalisar dokokin jihar Isam'il Falgore.
An dai amince da mutum 17 daga cikin mutum 19 da gwamnan jihar ya aike wa majalisar, in ban da Sheikh Tijjani Auwal da Hajiya Aisha Soji, waɗanda ba su halarci majalisar ba, sakamakon tafiyarsu aikin Hajji.
Bayan kammala tantance kwamshinonin, a yanzu hankali ya koma kan ma'aikatun da kwamshinonin za su jagoranta bayan an rantsar da su.
Comments
Post a Comment
Rubuta Sharhinku