#Attribution1 {display; none;} Skip to main content

Juma'a 23, Yuni, 2023

Muhuwi zai binciki Ganduje abubuwa hudu

Shugaban hukumar sauraron ƙorafe-ƙorafen al'umma da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano watau PCACC, Barista Muhuyi Magaji ya ce zai gudanar da wasu jerin bincike a kan tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje da gwamnatinsa.

Daya daga cikin binciken da shugaban na yaki da rashawa a Kano yace zai mayar da hankali a kai shi ne binciken 'bidiyon dala'.

A ranar Laraba ne gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya amince da mayar da Barista Muhuyi kan muƙaminsa nasa, bayan korarsa da tsohuwar gwamnatin jihar ta yi bisa dalilin cewa akwai shakku kan yanayin tafiyar da ayyukansa.

Sai dai kwana ɗaya bayan mayar da shi kan muƙamin, shugaban na PCACC ya shaida wa BBC cewar akwai wasu jerin zarge-zarge a kan gwamnatin Ganduje, waɗanda yake shirin buɗe bincike a kansu.

Ya ce "Za mu ɗora daga inda muka tsaya, dama akwai wasu bincike-bincike da muke yi wadanda daga baya wasu suke ganin ba za su yadda a ci gaba da yi ba saboda ya shafe su."

Lamarin ya fara tayar da ƙura ne bayan da Barista Muhuyi ya furta cewa hukumar 'za ta yi abin da ya kamata' a kan batun bidiyon zargin karɓar maƙudan kuɗaɗen dalar Amurka da ake yi wa tsohon gwamnan na jihar Kano.

Tun a lokacin da bidiyon ya fito, Ganduje ya musanta karbar rashawa inda yace siyasa ce kawai.

Sai dai ya ce ba bidiyon dala ne kawai zarge-zargen da ke kan tsohon gwamnan ba.

Bidiyon dala<\b>

Muhuyi Magaji ya ce ɗaya daga cikin manyan abin da zai mayar da hankali bayan komawa kan muƙaminsa shi ne binc

Comments

Popular posts from this blog

Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam

Wata kotu a Birtaniya ta samu ɗan majalisar dattijan Najeriya, Ike Ekweremadu da matarsa da laifin yunkurin safarar sassan ɗan adam. Shari'ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun. Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda. Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25. Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata. Matashin da aka so amfani da ƙodar tasa, wani mai ƙaramar sana’a ne a birnin Legas. An kai shi Birtaniya ne a bara domin gudanar da aiki a asibitin Royal Free Hospital da ke biornin London. Ya ce an yi alƙawarin samar masa aiki a Birtaniya saboda taimakon da zai yi, sai dai ya ce ya gane cewa ana masa shigo-shigo ba zurfi ne bayan tattaunawa da likitoci a ƙasar ta Birtaniya. Duk da cewa ba laifi ba ne bayar da g

DEEJARH BERVER ENTERPRISES

DAMA GARE KU MATA!!! DAMA GARE KU MATA MASU BUKATAR KOYON GIRKE-GIRKEN KWALAM DA MAKULASHE, KUNA ZAUNE TSAF DAGA CIKIN GIDAJENKU. DEEJARH BERVER TA SHIRYA TSAF DOMIN KOYO MUKU HADADDUN GIRKE-GIRKE, YADDA ZAKI SARRAFA ABINCI DA LEMOKA DA HADIN SALAD DA SNACKS HAR GUDA 40, TAMKAR KUNA GABANTA. ZA A GABATAR DA KOYARWAR TA CIKIN WAYOYIN HANNUNKU WATO TSARIN ONLINE LECTURE MAI DAUKE DA HOTON VIDEO DA RUBUTU DALLA-DALLA AKAN TA CIKIN MANHAJAR WHATSAPP DA TELEGRAM. KOWA NA DA DAMAR YIN TAMBAYA KO TATTAUNAWA DA MALAMA A SIRRANCE. KU DAI KU YI RIJISTA A YAU AKAN KUDI NAIRA 2,500 KACAL. ZA MU FARA KOYARWA RANAR 18 March, 202. DOMIN KARIN BAYANI KIRA WANNAN LAMBAR 09079274454

Jadawalin Lokutan Sahur Da Buda Baki A Birnin Kano