#Attribution1 {display; none;} Skip to main content

Juma'a 23, Yuni, 2023

Hukumar NBC a Nijeriya ta ci tarar gidan talabijin na Channels naira miliyan biyar

Hukumar da ke kula da gidajen rediyo da talabijin ta Nijeriya NBC ta maka wa gidan talabijin na Channels a kasar tarar naira miliyan biyar kan saba ka’idojin watsa labarai.

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito cewa NBC ta aika wa gidan talabijin din takardar tarar ne a sakamakon wani shiri na siyasa da aka yi da mataimakin dan takarar shugaban kasa a karkashin Jam’iyyar Labour Dr Datti Baba-Ahmed.

Takardar mai taken “Hirar tunzurarwa, saka takunkumi”, na dauke da sa hannun shugaban hukumar wato Balarabe Shehu Ilelah.

“Hukumar NBC ta kalli wata tattaunawa da aka yi kai tsaye da mataimakin dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Labour, Dakta Datti Baba-Ahmed, wadda jagoran shirin Politics Today, Seun Okinbaloye ya jagoranta a ranar Laraba, 22 ga watan Maris.

“Dakta Baba-Ahmed ya bayana cewa za a saba wa kundin tsarin mulki idan aka rantsar da zababben shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu, saboda kurakuran zabe,” in ji Ilelah a takardar.

Ya bayyana cewa wannan tattaunawar da aka yi za ta iya tunzura jama’a da tayar da zaune tsaye inda ya ce an saba wa wasu ka’idojin watsa labarai.

Ya ce hakan kuma ya hada sashen da ke cewa kada a watsa wani labari da zai iya tunzurawa ko kuma zai sosa zukatan jama’a ko kuma labaran na magana ne kan wani ko wata kungiya mai rai ko matacce ko kuma taba darajar bil adama.

Ya bayyana cewa sakamakon saba wadannan dokoki, gidan talabijin din zai biya N5,000,000 a karon farko.

Haka kuma ya ce duk wani abu irin wannan da ya sake biyowa baya zai jawo tarar da ta fi wannan. Darakta Janar din na NBC ya ba gidan talabijin din mako biyu ya biya wannan tarar ko kuma hukuncin ya zarta hakan.

Comments

Popular posts from this blog

Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam

Wata kotu a Birtaniya ta samu ɗan majalisar dattijan Najeriya, Ike Ekweremadu da matarsa da laifin yunkurin safarar sassan ɗan adam. Shari'ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun. Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda. Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25. Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata. Matashin da aka so amfani da ƙodar tasa, wani mai ƙaramar sana’a ne a birnin Legas. An kai shi Birtaniya ne a bara domin gudanar da aiki a asibitin Royal Free Hospital da ke biornin London. Ya ce an yi alƙawarin samar masa aiki a Birtaniya saboda taimakon da zai yi, sai dai ya ce ya gane cewa ana masa shigo-shigo ba zurfi ne bayan tattaunawa da likitoci a ƙasar ta Birtaniya. Duk da cewa ba laifi ba ne bayar da g

DEEJARH BERVER ENTERPRISES

DAMA GARE KU MATA!!! DAMA GARE KU MATA MASU BUKATAR KOYON GIRKE-GIRKEN KWALAM DA MAKULASHE, KUNA ZAUNE TSAF DAGA CIKIN GIDAJENKU. DEEJARH BERVER TA SHIRYA TSAF DOMIN KOYO MUKU HADADDUN GIRKE-GIRKE, YADDA ZAKI SARRAFA ABINCI DA LEMOKA DA HADIN SALAD DA SNACKS HAR GUDA 40, TAMKAR KUNA GABANTA. ZA A GABATAR DA KOYARWAR TA CIKIN WAYOYIN HANNUNKU WATO TSARIN ONLINE LECTURE MAI DAUKE DA HOTON VIDEO DA RUBUTU DALLA-DALLA AKAN TA CIKIN MANHAJAR WHATSAPP DA TELEGRAM. KOWA NA DA DAMAR YIN TAMBAYA KO TATTAUNAWA DA MALAMA A SIRRANCE. KU DAI KU YI RIJISTA A YAU AKAN KUDI NAIRA 2,500 KACAL. ZA MU FARA KOYARWA RANAR 18 March, 202. DOMIN KARIN BAYANI KIRA WANNAN LAMBAR 09079274454

Jadawalin Lokutan Sahur Da Buda Baki A Birnin Kano