Ministan kudi, kasafin kudi da kuma Tsare-tsare ta kasa, Zainab Ahmed, ta bayyana hakan a ranar Larabar da ta gabata, jim kadan bayan kammala taron majalisar zartaswa ta kasa (FEC) da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta.
A cewar Ahmed, gwamnatin Najeriya ta kuduri aniyar kawo karshen tallafin man fetur nan da watan Yuni, don haka ta fara wani yunkuri na rage wa ‘yan kasar damuwa. Ta yi nuni da cewa, tuni aka samu kyakkyawar alaka da sabuwar majalisar rikon kwarya ta shugaban kasa (PTC) da kuma gwamnati mai zuwa, da nufin tafiyar da shirin.
"Mun samu makudan kudade da suka kai dala miliyan 800 daga bankin duniya domin tafiyar da ayyukan jin kai, kuma muna tunkarar gidaje kusan miliyan 10 ko kuma 'yan Najeriya miliyan 50 masu rauni a matakin farko." In ji Ministan yayin da take zantawa da manema labarai a fadar gwamnatin jihar.
Ta lura cewa kaso mai yawa na kudaden zai kai ga gidaje miliyan 10 da ake ganin sun fi fama da rauni, don rage tasirin cire tallafin.
“A halin yanzu muna shigar da dukkan masu ruwa da tsaki. Mun san cewa ana yin la'akari da tsare-tsare daban-daban, gami da buƙatar motocin bas don ma'aikata, da wasu tsare-tsare da yawa na kwantar da hankali, ”in ji ta.
Comments
Post a Comment
Rubuta Sharhinku