#Attribution1 {display; none;} Skip to main content

Posts

Showing posts from April, 2023

Juma'a 23, Yuni, 2023

An ga watan Sallah a Najeriya

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa’ad III ya sanar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya. Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III ya ce ganin jinjirin watan da aka yi a a kasar ya sanya ranar Juma’a 21 ga watan Afrilu, 2023 ta zamo 1 ga watan Shawwal, 1444. Kwamitin tantance ganin wata karkashin jagorancin Maigirma Wazirin Sakkwato Farfesa. Sambo Wali Junaidu ne ya jagoranci aikin tabbatar da ganin watan a bana. Cikin sanarwar da ya yi Sarkin Musulmi ya ce "mun samu bayanai daga wurare daban-daban a Najeriya kuma mun zauna da masana domin tabbatar da ingancin waɗannan bayanan gabanin mu sanar da al'umma cewa an ga watan. Domin haka gobe Juma'a 21 ga watan Afrilu 2023 ita ce 1 ga watan Shawwal 1444," in ji Sarkin Musulmi. Ya yi kira ga sauran musulmin ƙasar da su ajiye azumi domin an ga wata, su kuma yi shirin zuwa masallaci domin halartar Sallar Idi a wurare daban-daban. Akasarin Musulmai a fadin duniya dai sun tashi da Azumin watan Ramadan ra

Sallah sai ranar Asabar a Iran

Ofishin Jagoran addinin na Iran Ali Khamenei ya sanar da cewa ba a ga jaririn watan Shawwal ba a ranar Alhamis 20 ga watan Afrilun 2023, don haka watan Ramadan zai ƙare ranar Juma'a 21 ga watan Afrikun, Asabar ta zama sallah 1 gawatan Shawwal. A cewar rahotanni kimanin ƙungiyoyi 100 aka aika yankuna mabambanta domin aikin ganin jaririn watan na Shawwal. Rahotannin sun ce wasu daga cikin waɗanda suka yi aikin duba watan a ƙauyen Qom yanayin duhun gari ne ya hana su ganin shi.

An ga watan Sallah a Saudiyya

Hukumomin Saudiyya sun sanar da ganin watan Shawwal na sallah a ranar Alhamis 20 ga watan Afrilun 2023. An ga watan ne a yankin Tumair na Saudiyya kamar yadda kwamitin duban wata na yankin ya bayyana, hakan na nufin Saudiyya ta kammala azumin Ramadan 29. Gobe Juma'a 21 ga watan Afrilu zai zama 1 ga watan Shawwal.

Juma'a 7 ga Afrilu, 2023

Juma'a 7 ga Afrilu, 2023

Kalaman Peter Obi sun yamutsa hazo a siyasar NajeriyaA Najeriya

Cacar-baki ta kaure tsakanin 'ya'yan jam'iyyar APC mai mulkin ƙasar da na jam'iyyar Labour mai adawa. Lamarin na zuwa ne, tun bayan jin wata tattaunawar wayar salula tsakanin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour, Peter Obi da Bishop David Oyedepo, wani babban limamin Kirista na majami'ar Living Faith Church. A ƙarshen mako ne, wata jaridar intanet mai suna People Gazette ta wallafa wannan murya da aka kwarmata, tsakanin Peter Obi da babban limamin Kiristan, Bishop David Oyedepo. Wannan ya janyo ce-ce-ku-ce da zazzafar muhawara a shafukan sada zumunta a ƙasar. Musamman ma yadda aka ji ɗan takarar yana roƙon malamin ya taimaka wajen nema masa goyon bayan mabiya addinin kirista da ke shiyyar kudu maso yammacin Najeriya da kuma shiyyar arewa ta tsakiyar ƙasar. Ya dai alaƙanta siyasar da takararsa, tamkar wata fafutukar yaƙi na addini, har ma ya tattabar wa limamin Kiristan da cewa ba za su yi da-na-sanin goya masa baya ba. `Yan jam`iyya

Kada Ku Sake Bai Wa Gwamnati Mai Barin Gado Bashi —Abba

Zababben gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya shawarci bankuna da su daina bai wa gwamnati mai barin gado bashi. Wannan dai na zuwa ne bayan shawarar da ya bai wa masu gine-gine a filayen gwamnati, makarantu, makabartu da sauransu. Yusuf ya bayar da wannan shawara kan gine-gine ba bisa ka’ida ba a wurare jama’a. Sai dai kuma gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ta ce ya daina zumudi ya bari a rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu. Amma a cikin wata shawara da ya sake barwa da ke kunshe cikin wata sanarwa dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran gwamnan mai jiran gado, Sanusi Bature Dawakin Tofa, Abba ya jadadda cewar cewa shawarar ta zama dole. Sanarwar ta ce: “Daga ranar 18 ga watan Maris zuwa 29 ga Mayu, babu wani mai ba da lamuni (na gida ko na waje) da zai amince da bayar da rance ga gwamnatin Jihar Kano ba tare da amincewar gwamnati mai zuwa ba. “Duk masu ba da rancen kudi ga Gwamnatin Jihar Kano su lura cewa gwamnati mai barin gado na cin bashi ba g

Obasanjo ya bukaci kotun Birtaniya ta sassauta wa Ekweremadu hukunci

Tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo ya rubuta wa jami'an kotu a Birtaniya , inda yake bukatar a yi sassauci lokacin yanke wa sanatan Najeriya Ike Ekweremadu da matarsa hukunci bayan kama su da laifin 'safarar sassan jikin ɗan bil'adama.' A watan da ya gabata ne kotu ta samu sanata Ike Ekweremadu mai shekara 60 da matarsa Beatrice da kuma wani likita Dr Obinna Obeta da laifin ɗaukar wani matashi ɗan shekara 21 daga Legas zuwa Birtaniya domin cire ƙodarsa, domin a bai wa ƴarsa Ekweremadu, mai suna Sonia, mai shekara 25. A wasikar da Obasanjo ya rubuta, ya ce abin da ma'auratan suka yi ba daidai ba ne kuma babu wata al'umma da za ta lamunci aikata hakan. Sai dai ya bukaci kotun da ta duba lamarin ƴar sanatan wadda lafiyarta ke cikin haɗari da kuma ke son agajin lafiya na gaggawa domin sassauta masa. Obasanjo ya kuma faɗa wa kotun cewa ta duba ɗabi'u masu kyau da Ekweremadu ke da su a lokacin yanke masa hukunci. Sai dai babu tabbacin cewa ko w

Zan yi nesa da Abuja idan na sauka daga mulki - Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce zai koma mahaifarsa Daura da ke jihar Katsina, idan ya miƙa ragamar mulki ga sabuwar gwamnati mai zuwa a ranar 29 ga watan Mayu. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Femi Adesina ya fitar, ya ce Buhari ya faɗi haka ne jiya Laraba lokacin da ya karɓi bakuncin Jakadiyar Birtaniya a Najeriya mai barin gado, Catriona Wendy Laing. Buhari ya yaba wa ƙasar Birtaniya kan tallafa wa Najeriya a ɓangarori da dama, musamman ma wajen sake gina yankin arewa maso gabas da ayyukan ƴan tayar da ƙayar-baya ya ɗaiɗaita. Ya ce Birtaniya ta kasance gida ga ƴan Najeriya da dama, inda ya ce dangataƙar ƙasashen biyu za ta ci gaba da wanzuwa. Tun da farko, Jakadiyar Birtaniyar ta ce ba ta jin daɗi barin Najeriya da za ta yi, musamman ma ganin cewa ta saba da abubuwa da dama a ƙasar, kamar al'adu da raye-raye da kuma wakokin ƴan ƙasar masu daɗi. Ta ce ta ji daɗin kasancewarta a Najeriya, inda ta ce ta ziyarci jihohi sama da 20. Ta ce "na

Yan mata 20,000 da aka aurar bara sun haifi jarirai 10,000 a Iran

'Yan mata fiye da 20,000 ne 'yan shekara 15, aka yi wa aure a cikin wata taran da ya gabata a ƙasar Iran, a cewar alƙaluman Cibiyar Ƙididdiga ta Ƙasar. A cewar alƙaluma da jaridar intanet ta Etemad ta wallafa, an kuma samu "sakin aure 179 a cikin 'yan matan 'yan ƙasa da shekara 15". Akwai 'yan mata 'yan ƙasa da shekara 15 da suka haifi jarirai 1,085. Cibiyar Ƙididdigar ta wallafa wannan rahoto ne a kan halin rayuwar zamantakewa da ta al'adar al'ummar Iran a cikin watanni ukun farkon shekara. A cewar dokokin kula da hulɗar jama'a na Iran, shekarun aure ga 'ya mace suna farawa ne daga 13, maza kuma daga shekara 15. Haka zalika, ana iya aurar da mutum wanda shekarunsa ba su cika ƙa'ida ba, bisa doka amma da sharaɗin yardar mahaifi ko wani mai kula da shi sannan sai kotu ta amince. Yunƙurin canza shekarun aure a majalisar dokokin Iran yana da dogon tarihi a ƙasar.

Kafa gwamnatin rikon kwarya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya ne — Hedikwatar Tsaro

Hedikwatar tsaro ta Najeriya ta bayyana kiran gwamnatin wucin gadi da wasu mutane ke yi a kasar a matsayin abin takaici da kuma saba wa kundin tsarin mulkin kasar. Darakta mai kula da ayyukan yada labarai na tsaro, Maj.-Gen. Musa Danmadami, ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a taron mako biyu kan ayyukan sojoji a fadin kasar nan ranar Alhamis a Abuja. Danmadami ya ce masu kira da a kafa gwamnatin rikon kwarya suna kokarin yin barna ne kawai, ya kara da cewa kundin tsarin mulkin kasar bai tanadar da gwamnatin wucin gadi ta kasa ba. Ya ce: “Akan batun gwamnatin wucin gadi, abin takaici ne. “An gudanar da zabe kuma Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, da aka bawa izini ta sanar da zababben shugaban kasa. “Ba alhakinmu ba ne mu yi magana a kan wannan batu amma na san cewa an yi kira da yawa daga fadar shugaban kasa cewa babu wani abu kamar gwamnatin wucin gadi ta kasa. "Don haka ina tsammanin mutane suna ƙoƙarin yin ɓarna ne kawai. Ya saba

‘Yan Arewa na shirin maye gurbin Tinubu da Shettima – Naja’atu Mohammed

Naja’atu Mohammed, ta bayyana shirin da ‘yan Arewa ke yi na maye gurbin dan takarar Shugaban kasa na Jam’iyyar APC, Bola Tinubu, da abokin takararsa, Kashim Shettima. Naja’atu ta yi ikirarin cewa wasu ’yan Arewa ne ke kira ga Tinubu ya ci gaba da cewa Shettima zai maye gurbinsa idan lafiyarsa ta tabarbare kuma ya gaza. Da take magana da jaridar ThisDay, Naja’atu ta ce: “Suna so ne kawai su tura shi ya zama shugaban kasa. Ko da bai dace da sha’awarsa ba.” “Wasu mutane daga Maiduguri sun kira ni yau suna tambayar, ‘Hajiya, me ya sa kika yi haka? Yanzu kina sukar kudirinmu. Danmu zai zama shugaban kasa, amma kina magana irin wannan? Bayan haka ma, yanzu dubi Tinubu; ba zai iya ba. Mu duka don Kashim muke yi. Ba ki kyautata mana ba.” Naja’atu ta kuma yi ikirarin cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari bai damu da tattalin arziki, tsaro, ko kuma wanda zai gaje shi a matsayin shugaban kasa ba. Ta bayyana cewa, duk da bayanan da aka samu daga dukkan hukumomin tsaro, shugaban bai damu da

Cire tallafin man fetur: Bankin Duniya ya baiwa FG $800m don bayar da tallafi

Babban Bankin Duniya ya ba wa gwamnatin Najeriya dala miliyan 800 domin ta samar da wani tsari mai inganci ga ‘yan kasarta, kafin a cire tallafin man fetur nan da watan Yunin 2023. Ministan kudi, kasafin kudi da kuma Tsare-tsare ta kasa, Zainab Ahmed, ta bayyana hakan a ranar Larabar da ta gabata, jim kadan bayan kammala taron majalisar zartaswa ta kasa (FEC) da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta. A cewar Ahmed, gwamnatin Najeriya ta kuduri aniyar kawo karshen tallafin man fetur nan da watan Yuni, don haka ta fara wani yunkuri na rage wa ‘yan kasar damuwa. Ta yi nuni da cewa, tuni aka samu kyakkyawar alaka da sabuwar majalisar rikon kwarya ta shugaban kasa (PTC) da kuma gwamnati mai zuwa, da nufin tafiyar da shirin. "Mun samu makudan kudade da suka kai dala miliyan 800 daga bankin duniya domin tafiyar da ayyukan jin kai, kuma muna tunkarar gidaje kusan miliyan 10 ko kuma 'yan Najeriya miliyan 50 masu rauni a matakin farko." In ji Ministan yayin da t

Hukumar NBC a Nijeriya ta ci tarar gidan talabijin na Channels naira miliyan biyar

Hukumar da ke kula da gidajen rediyo da talabijin ta Nijeriya NBC ta maka wa gidan talabijin na Channels a kasar tarar naira miliyan biyar kan saba ka’idojin watsa labarai. Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito cewa NBC ta aika wa gidan talabijin din takardar tarar ne a sakamakon wani shiri na siyasa da aka yi da mataimakin dan takarar shugaban kasa a karkashin Jam’iyyar Labour Dr Datti Baba-Ahmed. Takardar mai taken “Hirar tunzurarwa, saka takunkumi”, na dauke da sa hannun shugaban hukumar wato Balarabe Shehu Ilelah. “Hukumar NBC ta kalli wata tattaunawa da aka yi kai tsaye da mataimakin dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Labour, Dakta Datti Baba-Ahmed, wadda jagoran shirin Politics Today, Seun Okinbaloye ya jagoranta a ranar Laraba, 22 ga watan Maris. “Dakta Baba-Ahmed ya bayana cewa za a saba wa kundin tsarin mulki idan aka rantsar da zababben shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu, saboda kurakuran zabe,” in ji Ilelah a takardar. Ya bayyana cewa wannan t