#Attribution1 {display; none;} Skip to main content

Posts

Showing posts from June, 2023

Juma'a 23, Yuni, 2023

Juma'a 23, Yuni, 2023

Saudiyya ta samar da motoci marasa matuƙa don jigilar mahajjata

Saudiyya za ta ƙaddamar da motoci marasa matuƙa masu amfani da lantarki, da za su yi jigilar mahajja a aikin hajjin bana. Hukumar kula da sufurin ƙasar ta ce ta ɗauki matakin ne domin zamanantar da kuma sauƙaƙa harkar sufuri a ƙasar. Matakin na daga cikin yunƙurin da hukumomin ƙasar ke yi don faɗaɗa harkokin sufuri musamman a lokacin aikin hajjin bana. Sabbin motocin masu sarrafa kansu na ɗauke da kyamarori da wasu abubuwa da za su sanya su yin aiki da kansu ba tare da wata matsala ba. Motocin kan tattara bayanai a lokacin da suke aiki, tare da yin nazari a kan bayanan, domin ɗaukar mataki. Manyan motocin waɗanda ke da kujeru 11, za su iya yin gudun kilomita 30 a cikin sa'a ɗaya, kuma batirinsu zai iya riƙe chaji na tswon sa'o'i 6.

Majalisar Kano ta tantance kwamishinoni 17 a cikin 19 da gwamna ya aike mata

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da mutum 17 daga cikin sunaye 19 da gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf ya aike mata domin amincewa da naɗinsu a matsayin kwamishinoni a jihar. Majalisar ta amince da sunayen ne a zamanta na ranar Alhamis, ƙarƙashin jagorancin kakakin majalisar dokokin jihar Isam'il Falgore. An dai amince da mutum 17 daga cikin mutum 19 da gwamnan jihar ya aike wa majalisar, in ban da Sheikh Tijjani Auwal da Hajiya Aisha Soji, waɗanda ba su halarci majalisar ba, sakamakon tafiyarsu aikin Hajji. Bayan kammala tantance kwamshinonin, a yanzu hankali ya koma kan ma'aikatun da kwamshinonin za su jagoranta bayan an rantsar da su.

Jami'an tsaro na farautar 'yan bindigar da suka kashe mutum 15 a Plateau

Hukumomin jihar Plateau da ke tsakiyar Najeriya sun ce jami'an tsaro na neman 'yan bindigar da suka kai hare-hare kan wasu garuruwa biyu, tare da kashe a ƙalla mutum 15 a jihar. Rahotonni na cewa 'yan bindigar sun kashe wasu manoma shida a yankin Riyom, yayin da waso 10 suka rasa rayukansu a yankin Mangu ranar Talata. Maharan sun ƙaddamar da hari kan garuruwan biyu inda suka kashe mutane tare da cinna wuta kan gidaje masu yawa. Mai magana da yawun gwamnan jihar Mista Gyan Bere ya shaida wa BBC cewa an shirya tawagar jami'an tsaro da ta ƙunshi sojoji da 'yan sanda domin kare garuruwan tare da farauto maharan. Ya ƙara da cewa gwamnan jihar ya gaji irin waɗannna hare-hare ne daga tsohuwar gwamnatin jihar. ''Gwamna na ganawa da shugabannin tsaro da jagororin al'umma domin magance matsalar da ake ciki, da kuma maido da zaman lafiya a faɗin jihar'', in ji shi. Mista Bere ya ce gwamnatin jihar ba ta kai ga gano waɗanda ke kai hare-ha

Tinubu ya hallara a wurin taron harkokin kuɗi a Paris

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya isa dakin taron da za a gudanar da babban taron harkar kuɗaɗe da tallafawa ƙasashe masu rauni, da za a gudanar a birnin Paris. Shugaban ya samu tarbar ministar harkokin ƙasashen wajen Faransa da nahiyar Turai Catherine Colonna. Taron shi ne na farko da shugaban na Najeriya ke halarta tun bayan rantsar da shi a matsayin shugaban ƙasar ranar 29 ga watan mayun da ya gabata.

Atiku na gabatar da shaidu a kotun sauraron ƙararrakin zaɓen shugaban ƙasa

Kotun sauraron ƙararraƙin zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya ta ci gaba da zaman saurarorin ƙorafin jam'iyyar PDP da Atiku Abubakar, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar. A baya dai kotun ta ɗage zaman sauraron ƙararrakin zuwa yau Alhamis domin bai wa jam'iyyar damar gabatar da shaidunta. Jam'iyyar PDP da ɗan takarar tata Atiku Abubukar sun shigar da ƙara a gaban kotun domin kalubalantar nasarar da Bola Ahmed Tinubu na jam'iyyar APC. Hukumar zaɓen ƙasar INEC ce ta ayyana Bola Ahmed Tinubu na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar ranar 25 ga watan Fabrairu. Matakin da jam'iyyun adawa ciki har da PDP da LP suka ce ba su gamsu da shi ba. Lamarin da ya sa jam'iyun da 'yan takararsu suka garzaya kotun suna neman ta soke zaɓen da ya bai wa Tinubu nasara a zaɓen.

Muhuwi zai binciki Ganduje abubuwa hudu

Shugaban hukumar sauraron ƙorafe-ƙorafen al'umma da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano watau PCACC, Barista Muhuyi Magaji ya ce zai gudanar da wasu jerin bincike a kan tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje da gwamnatinsa. Daya daga cikin binciken da shugaban na yaki da rashawa a Kano yace zai mayar da hankali a kai shi ne binciken 'bidiyon dala'. A ranar Laraba ne gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya amince da mayar da Barista Muhuyi kan muƙaminsa nasa, bayan korarsa da tsohuwar gwamnatin jihar ta yi bisa dalilin cewa akwai shakku kan yanayin tafiyar da ayyukansa. Sai dai kwana ɗaya bayan mayar da shi kan muƙamin, shugaban na PCACC ya shaida wa BBC cewar akwai wasu jerin zarge-zarge a kan gwamnatin Ganduje, waɗanda yake shirin buɗe bincike a kansu. Ya ce "Za mu ɗora daga inda muka tsaya, dama akwai wasu bincike-bincike da muke yi wadanda daga baya wasu suke ganin ba za su yadda a ci gaba da yi ba saboda ya shafe su." Lamarin ya fara tay